ALLAH YA JIKAN IYAN ZAZZAU ALHAJI DR BASHIR AMINU OON
https://www.facebook.com/groups/550204751780665/permalink/2159607834173674/
ALAH YA GAFARTA MAI DA RAHAMA
MAY HIS JENTLE SOUL CONTINUE TO REST IN JANNATUL FIRDAUSI
TARIHIN MAIGIRMA IYAN ZAZZAU
(Iya @ 70 years)
An Haifi Alh. Bashir Aminu Iyan Zazzau a 26th December 1950 a rimin tsiwa dake birnin Zaria. Maigirma Iyan Zazzau Da ne wajen marigayi Maimartaba Sarkin Zazzau Mal. Muhammad Aminu daga gidan Sarautar Katsinawa a Zazzau.
Yayi Karatun Allo (Alqur'ani) da na Addini a birnin Zaria. Ya shiga makarantar Kwaleji ta Alhuda Huda dake kofar Doka Zaria daga shekara ta 1964 - 1968. Ya shiga Kaduna Polytechnic inda ya sami Diploma a Accounting And Auditing daga shekara ta 1970 - 1971. Ya shiga Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria yayi Digiri a Accounting a shekara ta 1972 - 1975. Ya ketara kasar Ingila Jami'ar Kent Canterbury domin yin Masters a M. SC Finance a shekara ta 1982.
Maigirma Iyan Zazzau yayi aiki da Gwamnatin Jahar Kaduna a matsayin Accountannt daga 1970 - 1975.
Yayi aiki a kaduna state Polytechnic a matsayin Chief Finance Officer daga 1976 - 1979
Marigayi Maimartaba Sarkin Zazzau Alh. Dr. Shehu Idris CFR Allah ya gafarta masa yayi ma Alh. Bashir Aminu Sarautar Iyan Zazzau a 23rd Febuary, 1979 kuma hakimin Sabon Gari Zaria.
Iyan Zazzau ya Zama Shugaba a Boards of both state and Federal Government Parastatals and Companies tun shekaran 1980. Ya zama Shugaba a Board of Aviation technology Zaria, Jahar kaduna kar kashin Ma'aikatar Aviation ta Kasa daga shekara ta 1990 - 1994.
Ya zama Darakta a kamfanoni Da da yawa a fadin Nigeria.
Ya Halarci Samina Kala kala a kasar Nigeria da kasashen waje Kamar Ingila, Amerika da shauran kasashe.
Yana da mata 4 sannan ya haifi yaya maza da mata guda 33 biyu sun rasu saura 31
Allah ya gafarta mai da rahama Allah ya jikansa yasa ya huta
(R I J F)IYAN ZAZZAU
Rashid Abubakar ✍️
#26December2020
Reviewed by SAMSONGALAXY.com
on
3:16 AM
Rating:



No comments: