Facebook zai samar da intanet mai arha a Afrika
Kamfanin sada zumunta na Facebook ya bayyana cewa hannun jarin da ya zuba kan intanet zai jawo wa nahiyar haɓakar tattalin arziƙi da kusan dala biliyan 60 zuwa 2024.
A wani rahoto da kamfanin ya fitar, ya bayyana cewa ƙaruwar mutane a shiga intanet zai sa kuɗin intanet ɗin ya ragu a nahiyar.
Kamfanin na Facebook ya ce yana zuba kuɗi wurin samar da kayayyakin haɓaka intanet ɗin wanda hakan zai bada dama ga mutane masu zama a kudu da hamadar sahara su samun intanet cikin sauƙi.
A halin yanzu, kamfani na Facebook ya samar da wi-fi ta intanet a ƙasashe bakwai ga kusan mutum miliyan huɗu a Uganda da Najeriya.
Sama da rabin mutanen da ke kudu da hamadar sahara ba su da damar shiga intanet, kuma intanet ɗin na da tsada idan aka haɗa da sauran nahiyoyi.
Facebook zai samar da intanet mai arha a Afrika
Reviewed by SAMSONGALAXY.com
on
1:52 PM
Rating:
Reviewed by SAMSONGALAXY.com
on
1:52 PM
Rating:

No comments: